A Zeno.FM Station Ƴan bindiga sun kashe masallata 13 a Katsina Skip to main content

Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya

 Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya Kasashen Burkina Faso da Mali sun kaurace wa babban taron shugabannin sojojin Afirka da Najeriya ta shirya a Abuja, lamarin da ya nuna rashin jituwar diflomasiyya tsakanin kasashen Sahel masu mulkin soja da makwabtansu. Sai dai Nijar ce kadai daga cikin kasashen Alliance of Sahel States (AES) da ta halarci taron, inda jakadarta mai kula da harkokin tsaro, Colonel Major Soumana Kalkoye, ya wakilta ta. Babban Hafsan Sojin Najeriya, Christopher Musa, ya bukaci sabon tsarin hadin gwiwa na tsaro karkashin jagorancin Afirka, yana mai cewa kalubalen tsaro “ba su da iyaka” kuma dole a fuskance su tare. Najeriya da Nijar sun taba samun sabani bayan juyin mulkin 2023, amma daga baya suka rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro.  Sai dai janyewar Nijar daga rundunar hadin gwiwa ta yankin ya kawo cikas ga yaki da ’yan ta’adda a yankin Tafkin Chadi.

Ƴan bindiga sun kashe masallata 13 a Katsina

Ƴan bindiga sun kashe masallata 13 a Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da cewa ’yan bindiga sun kashe mutane 13 a yayin sallar Asuba ranar Talata, a wani harin ramuwar gayya da suka kai Unguwar Mantau a karamar hukumar Malumfashi.

Kakakin ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida na jihar, Dr. Nasir Muazu, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Katsina.

Ya ce, “Lamarin ya faru ne lokacin da miyagu suka kai hari domin ramuwar gayya a kan al’ummar garin. Mambobin al’umma Musulmi na cikin masallaci suna yin sallar Asuba, sai waɗannan ’yan ta’adda suka fara harbe-harbe cikin masallacin.”

Kwamishinan ya kara da cewa harin ramuwar gayya ne kan yadda al’ummar unguwar suka yi nasarar dakile su a kwana biyu da suka gabata.

A cewarsa, mutanen Unguwar Mantau sun yi wa ’yan bindigar kwanton bauna inda suka kashe da dama daga cikinsu.

Bayan wannan mummunan lamari, Muazu ya bayyana cewa jami’an tsaro sun isa yankin domin dawo da zaman lafiya.

Ya ce, “Kwamandan bangaren sojojin sama na FOB da kuma ’yan sandan Najeriya sun isa wajen domin kawar da wadannan ’yan bindiga. A lokacin damina, ’yan bindiga kan ɓuya a cikin amfanin gona domin aiwatar da munanan hari. Muna aiki tukuru domin ganin mun kamo su tare da hukunta su.”

Gwamnatin jihar ta yaba da jarumtar al’ummar Unguwar Mantau, tare da bayyana aniyar ta na ci gaba da yaki da ’yan bindiga da tabbatar da tsaro a dukkan al’ummomi.

“Hakika gwamnati na mika ta’aziyya ga iyalan wadanda abin ya shafa,” in ji Muazu.



Comments

Popular posts from this blog

Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya

 Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya Kasashen Burkina Faso da Mali sun kaurace wa babban taron shugabannin sojojin Afirka da Najeriya ta shirya a Abuja, lamarin da ya nuna rashin jituwar diflomasiyya tsakanin kasashen Sahel masu mulkin soja da makwabtansu. Sai dai Nijar ce kadai daga cikin kasashen Alliance of Sahel States (AES) da ta halarci taron, inda jakadarta mai kula da harkokin tsaro, Colonel Major Soumana Kalkoye, ya wakilta ta. Babban Hafsan Sojin Najeriya, Christopher Musa, ya bukaci sabon tsarin hadin gwiwa na tsaro karkashin jagorancin Afirka, yana mai cewa kalubalen tsaro “ba su da iyaka” kuma dole a fuskance su tare. Najeriya da Nijar sun taba samun sabani bayan juyin mulkin 2023, amma daga baya suka rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro.  Sai dai janyewar Nijar daga rundunar hadin gwiwa ta yankin ya kawo cikas ga yaki da ’yan ta’adda a yankin Tafkin Chadi.

Fiye da mutum miliyan 1.9 ne suka nemi aikin shiga cikin Hukumar Tsaro ta Fararen Hula (Civil Defence), Hukumar Shige da Fice (Immigration), Hukumar Gyaran Hali (Correctional Service), da kuma Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya (Federal Fire Service).

  Rahotanni sun nuna cewa daga cikin wannan adadi, mutum dubu 30 ne kawai za a dauka aiki. Dangane da yadda masu neman aikin suka rabu, Jihar Kogi ce ke da mafi yawan masu nema, inda suka kai fiye da mutum 116,000. Haka zalika, Jihar Kaduna na da fiye da mutum 114,000, Benue na da mutum 110,000 yayin da Jihar Kano ke da fiye da mutum 89,000. Rahoton ya kuma nuna cewa Jihar Katsina na da fiye da mutum 76,000, yayin da Jihar Nasarawa da Oyo suka haura mutum 67,000 kowannensu. Sannan, Jihar Kebbi da Jigawa suna da mutum 34,000 da 44,000 bi da bi. Baya ga haka, Babban Birnin Tarayya Abuja na da fiye da mutum 30,000 da suka nemi aikin, yayin da Jihar Legas ta yi rajistar mutum fiye da 14,000. Sai dai jihar da ta fi kankanta wajen yawan masu neman aikin ita ce Jihar Bayelsa, inda mutum 11,669 ne kacal suka nemi aiki a cikin wadannan hukumomin tsaron.

Majalissar Dokokin Jihar Katsina Ta Nemi A Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Matazu Da Sabuwa

  Majalisar Dokokin Jihar Katsina ta yi kira ga Gwamnatin Jiha da ta Tarayya da su ɗauki matakan gaggawa kan ƙara ta’azzarar matsalar tsaro a Matazu, Sabuwa da wasu yankuna. A zaman majalisar na ranar Litinin 11/08/2025, ƙarƙashin jagorancin Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura, Majalisar ta amince da ƙudurin ƙara yawan jami’an tsaro, musamman a Tashar Bawa da sauran wuraren da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga. Ƙudurin ya fito ne daga Hon. Ibrahim Umar Dikko na Matazu da Hon. Ibrahim Danjuma Machika na Sabuwa, inda suka nuna damuwa kan kashe-kashe, barin gidaje da hana manoma noma sakamakon harin  ƴan fashin Daji. Sun kuma nuna damuwa da janyewar jami’an tsaro daga wasu ƙauyuka. ‘Yan majalisa daga wasu mazaɓu sun goyi bayan ƙudurin tare da buƙatar a dawo da jami’an tsaro da inganta haɗin gwiwa don dawo da zaman lafiya. Shugaban Majalisar ya jaddada buƙatar ɗaukar matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi a duk faɗin jihar.