Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya Kasashen Burkina Faso da Mali sun kaurace wa babban taron shugabannin sojojin Afirka da Najeriya ta shirya a Abuja, lamarin da ya nuna rashin jituwar diflomasiyya tsakanin kasashen Sahel masu mulkin soja da makwabtansu. Sai dai Nijar ce kadai daga cikin kasashen Alliance of Sahel States (AES) da ta halarci taron, inda jakadarta mai kula da harkokin tsaro, Colonel Major Soumana Kalkoye, ya wakilta ta. Babban Hafsan Sojin Najeriya, Christopher Musa, ya bukaci sabon tsarin hadin gwiwa na tsaro karkashin jagorancin Afirka, yana mai cewa kalubalen tsaro “ba su da iyaka” kuma dole a fuskance su tare. Najeriya da Nijar sun taba samun sabani bayan juyin mulkin 2023, amma daga baya suka rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro. Sai dai janyewar Nijar daga rundunar hadin gwiwa ta yankin ya kawo cikas ga yaki da ’yan ta’adda a yankin Tafkin Chadi.
Ƴan Nijeriya 69,376 ne su ka cike matakin farko na rijistar katin zaɓe ta yanar-gizo a awanni 7 da buɗe shafin - INEC
Ƴan Nijeriya 69,376 ne su ka cike matakin farko na rijistar katin zaɓe ta yanar-gizo a awanni 7 da buɗe shafin - INEC Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce ta samu mutane 69,376 da suka yi rajistar farko ta yanar-gizo cikin awa bakwai kacal tun bayan da ta sake buɗe shafin ci gaba da yin rijistar katin zaɓe a fadin ƙasa. Kwamishinan INEC na ƙasa, Sam Olumekun, ya ce rajistar ta fara aiki da karfe 8:30 na safe a ranar Litinin, inda zuwa 3:30 na rana aka samu wannan adadi. Daga cikin su, maza sun kai 33,803, mata kuma 35,573, yayin da matasa masu shekaru 18 zuwa 34 suka kai sama da kashi 69%. Ya bayyana cewa rajistar kai tsaye ta mutum za ta fara ranar 25 ga Agusta a ofisoshin INEC 811 a fadin jihohi da kananan hukumomi, daga karfe 9 na safe zuwa 3 na rana a ranakun aiki. INEC za ta rika fitar da rahoton mako-mako kan yadda ake gudanar da rijistar, ciki har da bayanai kan jihohi, jinsi, shekaru da sana'a. Hukumar ta kuma jaddada cewa rajista ta buɗe ne kawai ...