Ƴan Nijeriya 69,376 ne su ka cike matakin farko na rijistar katin zaɓe ta yanar-gizo a awanni 7 da buɗe shafin - INEC
Ƴan Nijeriya 69,376 ne su ka cike matakin farko na rijistar katin zaɓe ta yanar-gizo a awanni 7 da buɗe shafin - INEC
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce ta samu mutane 69,376 da suka yi rajistar farko ta yanar-gizo cikin awa bakwai kacal tun bayan da ta sake buɗe shafin ci gaba da yin rijistar katin zaɓe a fadin ƙasa.
Kwamishinan INEC na ƙasa, Sam Olumekun, ya ce rajistar ta fara aiki da karfe 8:30 na safe a ranar Litinin, inda zuwa 3:30 na rana aka samu wannan adadi.
Daga cikin su, maza sun kai 33,803, mata kuma 35,573, yayin da matasa masu shekaru 18 zuwa 34 suka kai sama da kashi 69%.
Ya bayyana cewa rajistar kai tsaye ta mutum za ta fara ranar 25 ga Agusta a ofisoshin INEC 811 a fadin jihohi da kananan hukumomi, daga karfe 9 na safe zuwa 3 na rana a ranakun aiki.
INEC za ta rika fitar da rahoton mako-mako kan yadda ake gudanar da rijistar, ciki har da bayanai kan jihohi, jinsi, shekaru da sana'a.
Hukumar ta kuma jaddada cewa rajista ta buɗe ne kawai ga ‘yan Najeriya masu shekaru 18 da sama waɗanda ba su taɓa yin rajista ba, yayin da sauya rajista da maye gurbin kati da ya ɓata ko ya lalace.

Comments
Post a Comment