Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta kama tsohon gwamnan Jihar Sokoto, kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu, Aminu Waziri Tambuwal, bisa zargin zambar kuɗin jama’a da suka kai naira biliyan 189.
Tambuwal dai ya isa hedkwatar EFCC da ke Abuja da misalin karfe 11:30 na safiyar din nan Litinin, inda aka yi masa tambayoyi kan mu’amalolin da ake zargin sun saɓa wa dokar "Money Laundering" (Prevention & Prohibition) Act, 2022.
Wata majiya daga EFCC ta ce ana binciken kundaye na fitar da kuɗaɗe da ake kyautata zaton ba su da tushe. Kakakin hukumar, Dele Oyewale, ya ce za a fitar da cikakken bayani bayan kammala binciken.
Tambuwal ya yi gwamna daga 2015 zuwa 2023, kuma kafin haka ya kasance kakakin majalisar wakilai na tarayyar Nijeriya.

Comments
Post a Comment