A Zeno.FM Station Rundunar Yan Sanda Ta Jihar Katsina Ta Chafke Masu Laifuka Daban-Daban Su 302 A Cikin Watan Juli Skip to main content

Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya

 Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya Kasashen Burkina Faso da Mali sun kaurace wa babban taron shugabannin sojojin Afirka da Najeriya ta shirya a Abuja, lamarin da ya nuna rashin jituwar diflomasiyya tsakanin kasashen Sahel masu mulkin soja da makwabtansu. Sai dai Nijar ce kadai daga cikin kasashen Alliance of Sahel States (AES) da ta halarci taron, inda jakadarta mai kula da harkokin tsaro, Colonel Major Soumana Kalkoye, ya wakilta ta. Babban Hafsan Sojin Najeriya, Christopher Musa, ya bukaci sabon tsarin hadin gwiwa na tsaro karkashin jagorancin Afirka, yana mai cewa kalubalen tsaro “ba su da iyaka” kuma dole a fuskance su tare. Najeriya da Nijar sun taba samun sabani bayan juyin mulkin 2023, amma daga baya suka rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro.  Sai dai janyewar Nijar daga rundunar hadin gwiwa ta yankin ya kawo cikas ga yaki da ’yan ta’adda a yankin Tafkin Chadi.

Rundunar Yan Sanda Ta Jihar Katsina Ta Chafke Masu Laifuka Daban-Daban Su 302 A Cikin Watan Juli

 


Rundunar Yan Sanda Ta Jihar Katsina a karkashin jagorancin Kwamishina Bello Shehu ta samu nasarar kama masu laifuka daban-daban har su 302 a cikin Watan Juli na wannan shekarar da muke ciki.


Kakakin Rundunar DSP Abubakar Sadiq Aliyu ne ya tabbatar da hakan ga Manema Labarai a Hedikwatar Rundunar da ke Katsina,kuma Accuracy News Hausa ta shaida.


Kamar yadda ya bayyana,masu aikata laifukan da aka kama sun hada da wadanda ake zargi da aikata laifin fashi da makami su 14 da wadanda ake zargi da aikata laifin kisan kai su 22 sai masu laifin fyade su 25.


Haka zalika,Rundunar ta chafke wadanda ake zargi da aikata laifin satar kayan Gwamnati su 20 da masu laifin yadara su 2 da masu laifin safara da sayar da miyagun kwayoyi su 26.


Bugu da kari,akwai masu aikata laifuk daban-daban har su 194,wadanda ba'a ambata ba a cikin wancan rukunin na masu aikata laifukan.


Baya ga wannan, rundunar ta kuma samu nasarar kwato dabbobi 199 da ɓarayin shanu suka sata,sai kuma mutane sama da 50 da aka samu nasarar cetowa daga masu garkuwa da mutane.


Kayayyakin da aka samu daga wadanda ake zargin sun hada da mashina 2 da aka sata da motoci 3 sai kuma tulin miyagun kwayoyi da dai sauran su.


Accuracy News Hausa ta tsinkayi Kakakin Rundunar DSP Abubakar Sadiq yana mai danganta nasarorin bisa ga jajircewar jami'an rundunar,bisa ga hadin kai da suke samu daga Kwamishina Bello Shehu.


Ya kuma yabawa Gwamnatin Jihar Katsina da al'ummar Jihar,bisa ga goyon baya da hadin kai da suke baiwa rundunar,sai ya yi rokon karin hakan.


Daga karshe ya yi kira ga al'ummar Jihar Katsina akan koda yaushe su rika sanar da Ofishin Yan Sanda mafi kusa duk wani abinda basu aminta da shi ba,domin daukar matakin da ya kamata.


Za'a Iya Kiran Lambobin Waya Kamar Haka,Domin Samun Daukin Rundunar:


*0815697777722

*0902220969033

*07072722539

Comments

Popular posts from this blog

Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya

 Burkina Faso da Mali sun ƙaurace wa taron hafsoshin soji na Afirka da ke gudana a Najeriya Kasashen Burkina Faso da Mali sun kaurace wa babban taron shugabannin sojojin Afirka da Najeriya ta shirya a Abuja, lamarin da ya nuna rashin jituwar diflomasiyya tsakanin kasashen Sahel masu mulkin soja da makwabtansu. Sai dai Nijar ce kadai daga cikin kasashen Alliance of Sahel States (AES) da ta halarci taron, inda jakadarta mai kula da harkokin tsaro, Colonel Major Soumana Kalkoye, ya wakilta ta. Babban Hafsan Sojin Najeriya, Christopher Musa, ya bukaci sabon tsarin hadin gwiwa na tsaro karkashin jagorancin Afirka, yana mai cewa kalubalen tsaro “ba su da iyaka” kuma dole a fuskance su tare. Najeriya da Nijar sun taba samun sabani bayan juyin mulkin 2023, amma daga baya suka rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro.  Sai dai janyewar Nijar daga rundunar hadin gwiwa ta yankin ya kawo cikas ga yaki da ’yan ta’adda a yankin Tafkin Chadi.

Fiye da mutum miliyan 1.9 ne suka nemi aikin shiga cikin Hukumar Tsaro ta Fararen Hula (Civil Defence), Hukumar Shige da Fice (Immigration), Hukumar Gyaran Hali (Correctional Service), da kuma Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya (Federal Fire Service).

  Rahotanni sun nuna cewa daga cikin wannan adadi, mutum dubu 30 ne kawai za a dauka aiki. Dangane da yadda masu neman aikin suka rabu, Jihar Kogi ce ke da mafi yawan masu nema, inda suka kai fiye da mutum 116,000. Haka zalika, Jihar Kaduna na da fiye da mutum 114,000, Benue na da mutum 110,000 yayin da Jihar Kano ke da fiye da mutum 89,000. Rahoton ya kuma nuna cewa Jihar Katsina na da fiye da mutum 76,000, yayin da Jihar Nasarawa da Oyo suka haura mutum 67,000 kowannensu. Sannan, Jihar Kebbi da Jigawa suna da mutum 34,000 da 44,000 bi da bi. Baya ga haka, Babban Birnin Tarayya Abuja na da fiye da mutum 30,000 da suka nemi aikin, yayin da Jihar Legas ta yi rajistar mutum fiye da 14,000. Sai dai jihar da ta fi kankanta wajen yawan masu neman aikin ita ce Jihar Bayelsa, inda mutum 11,669 ne kacal suka nemi aiki a cikin wadannan hukumomin tsaron.

Majalissar Dokokin Jihar Katsina Ta Nemi A Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Matazu Da Sabuwa

  Majalisar Dokokin Jihar Katsina ta yi kira ga Gwamnatin Jiha da ta Tarayya da su ɗauki matakan gaggawa kan ƙara ta’azzarar matsalar tsaro a Matazu, Sabuwa da wasu yankuna. A zaman majalisar na ranar Litinin 11/08/2025, ƙarƙashin jagorancin Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura, Majalisar ta amince da ƙudurin ƙara yawan jami’an tsaro, musamman a Tashar Bawa da sauran wuraren da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga. Ƙudurin ya fito ne daga Hon. Ibrahim Umar Dikko na Matazu da Hon. Ibrahim Danjuma Machika na Sabuwa, inda suka nuna damuwa kan kashe-kashe, barin gidaje da hana manoma noma sakamakon harin  ƴan fashin Daji. Sun kuma nuna damuwa da janyewar jami’an tsaro daga wasu ƙauyuka. ‘Yan majalisa daga wasu mazaɓu sun goyi bayan ƙudurin tare da buƙatar a dawo da jami’an tsaro da inganta haɗin gwiwa don dawo da zaman lafiya. Shugaban Majalisar ya jaddada buƙatar ɗaukar matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi a duk faɗin jihar.